Jiya Laraba kwamitin sulhun MDD ya shirya wani taron muhawara a bainar jama'a karkashin jagorancin kasar Sin wadda ke rike da shugabancin karba karba na kwamitin na wannan wata, domin tattauna batutuwan da suka shafi wanzar da zaman lafiya da tabbatar da tsaro a nahiyar Afirka.
An shirya wannan taro ne domin sa kaimi ga kasashen duniya su kara samar da goyon baya ga kasashen Afirka wajen kara karfafa aikin wanzar da zaman lafiya da kuma tabbatar da tsaro a nahiyar Afirka baki daya. Babban sakataren MDD Antonio Guterres da kwamishinan kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU mai kula da harkokin zaman lafiya da tsaro Smail Chergui da sauran manyan jami'ai ne suka halarci taron.
Zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana a yayin taron cewa, kokarin da kwamitin sulhun MDD yake yi domin jawo hankalin kasashen duniya da su kara samar da goyon baya ga kasashen Afirka, musamman ma wajen tabbatar da zaman lafiya da kuma tsaro, zai kara ciyar da zaman lafiya da tsaro gaba a duk fadin duniya. Yana mai cewa, "Batun zaman lafiya da tsaro batu ne da ya sha dukkan yankunan kasa da kasa, don haka tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Afirka ya shafi muradun al'ummomin kasashen duniya baki daya, saboda haka hakki ne mai muhimmanci na kwamitin sulhun MDD."