Shugaba Xi Jinping ya bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin ganawar sa da shugaban Palasdinawa Mahmoud Abbas. Ya ce samar da kasashe biyu masu cin gashin kan su, masu iyakoki da aka shata tun a shekarar 1967, da kasar Palasdinawa mai helkwata a gabashin birnin kudus ita ce hanya mafi dacewa ta cimma nasarar da ake fata. (Saminu)