in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Eritrea ya gana da tawagar sada zumunta ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin
2017-07-16 13:25:46 cri
Kwanan baya shugaban kasar Eritrea Isaias Afewerki, ya gana da tawagar sada zumunta ta jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin a birnin Asmara, wadda ke karkashin jagorancin wani babban jami'in jam'iyyar mai suna Cui Shaopeng. Isaias ya bayyana fatansa na inganta hadin-gwiwa tare da kasar Sin, domin kara yin mu'amala a harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya.

A nasa bangaren, Cui Shaopeng ya isar da sakon gaisuwa na shugaban kasar Sin Xi Jinping zuwa ga Isaias, ya kuma ce, kasar Sin na son kara yin cudanya da hadin-gwiwa tare da jam'iyyar PFDJ mai mulkin kasar Eritrea, a wani kokari na ci gaba da raya hulda tsakanin kasashen biyu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China