A yau Jumma'a ne shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar Sin wato CPPCC Mr. Yu Zhengsheng, ya gana da mataimakin shugaban kasar Ghana Mahamudu Bawumia a nan Beijing.
A yayin ganawar tasu mista Yu ya ce, kasar Sin na fatan ci gaba da hada kai da Ghana, wajen kara azama ga hadin gwiwar abokantaka a tsakaninsu, a kokarin kara sada daukacin al'ummun kasashen biyu da alherai.
Shi kuwa a nasa bangare mista Bawumia ya ce, kasarsa na da burin koyi daga fasahohin kasar Sin a fannin raya kasa, da shiga ayyuka da shawarar "ziri daya da hanya daya" ta shafa, da zurfafa hadin gwiwa a tsakaninta da kasar Sin a fannoni daban daban, a wani mataki na daga matsayin huldar da ke tsakanin kasashen 2 zuwa sabon mataki. (Tasallah Yuan)