in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da gasar yin bayani ta Sinanci ta daliban kasashen Afirka karo na farko
2017-06-16 20:16:53 cri

An gudanar da gasar yin bayani ta Sinanci ta daliban kasashen Afirka karo na farko a ranar 13 ga wata a nan birnin Beijing, inda dalibai 15 daga kasashen Kenya, Congo Brazzaville, Senegal, Equatorial Guinea, Togo da sauransu suka yi bayani game da labarinsu a lokacin da suke kasar Sin.

Kamfanin CRBC na kasar Sin shi ne ya dauki nauyin karatun dukkan daliban zuwa nan kasar Sin da suka halarci gasar, wadanda suke karatu a jami'o'in koyon ilmin sufuri na Beijing, da na Chang'an, da na kimiyya da fasaha na Changsha. Karkashin shirin hadin gwiwar horar da kwararru a tsakanin Sin da Afirka, ya zuwa yanzu, kamfanin CRBC ya samar da kudi ga dalibai 291 daga kasashe 6 na Afirka wato Kenya, Congo Brazzaville, Senegal, Equatorial Guinea, Angola da Togo da su zo kasar Sin su yi karatu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China