in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya gana da ministan harkokin wajen kasar Japan
2017-05-31 13:35:03 cri
A jiya Talata ne, memban majalisar gudanarwar kasar Sin Yang Jiechi ya gana da ministan harkokin wajen kasar Japan Fumio Kisida a birnin Tokyo na kasar Japan.

A jawabinsa, Yang Jiechi ya yi nuni da cewa, kamata ya yi Sin da Japan su yi tunanin koyon darussan da suka faru a baya tare da hange makoma ta gaba, da rike dama da fadada hadin gwiwarsu da warware matsalolinsu, da raya dangantakarsu yadda ya kamata bisa tushen takardun siyasa 4 na kasashen biyu da ka'idoji hudu da suka cimma daidaito a kai.

Yang Jiechi ya jaddada cewa, ya kamata Sin da Japan su daidaita batun tarihi da batun yankin Taiwan da sauran batutuwan dake shafar tushen siyasa na dangankatar dake tsakanin kasashen biyu, da tabbatar da tushen siyasarsu.

A nasa bangare, Fumio Kisida ya bayyana cewa, Japan tana fatan raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin. Japan tana son kara yin mu'amala da juna da yin imani da juna a fannin siyasa, da zurfafa hadin gwiwarsu da sada zumunta a tsakanin jama'ar kasashen biyu.

Daga bisani bangarorin biyu sun yi musayar ra'ayoyi kan batun nukiliya na zirin Koriya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China