Ranar 29 ga watan Mayu rana ce ta dimokuradiyya a Nigeria, kuma a bana ne take cika shekaru 18 na kawo karshen mulkin soja a kasar. Sabili da haka ne mambobin wata kungiya mai zaman kanta dake rajin tabbatar da tsarin dimokuradiyya ta kasa da kasa a Nigeria, suka shirya bikin murnar wannan rana.