in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ICC ta yi gargadi game da yawaitar tashin hankali a CAR
2017-05-24 11:14:53 cri
Babbar mai shigar da kara a kotun hukunta manyan laifukan yaki ta kasa da kasa Fatou Bensouda, ta gargadi daidaikun jama'a da kungiyoyi dake kaddamar da hare hare kan fararen hula, da jami'an wanzar da zaman lafiya, da masu bada agaji a jamhuriyar tsakiyar Afrika CAR, da su guji wannan danyen aiki, kana ya jaddada cewa za'a zakule masu aikata wadannan laifuka domin gurfanar da su a gaban shari'a.

A watan da ya wuce, an sha samun yawaitar tashe-tashen hankula tsakanin kungiyoyi masu dauke da makamai a sassan CAR. Halin da ake ciki a yanzu babban tashin hankali ne sakamakon rahoton da aka samu game da zarge-zargen cin zarafi da kaddamar da hare-hare kan fararen hula da jami'an aikin wanzar da zaman lafiya, da masu aikin jin kai a kasar. Wadannan jerin laifuka sun kunshi irin laifukan dake karkashin hurumin ICC, don haka dole ne a dakatar da su, in ji Bensouda.

Ta ce, ofishinta yana bibiyar wadannan al'amurra tare da yin nazari game da irin matakan da ya dace a dauka a nan gaba. Ta ce a shirye suke su tallafawa hukumomin CAR wadanda suke da babban nauyi a wuyansu, na farko shi ne dole su gudanar da bincike kuma su garfanar da wadanda ake zargi da aikata laifukan a gaban shari'a. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China