in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira da a kara kokarin daidaita matsalar jin kai
2017-05-24 11:10:27 cri
A yayin cikar shekara guda da taron kolin harkokin jin kai na duniya, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya fitar da sanarwa a jiya Talata, inda ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa su ci gaba da kokarin magance tare da kawo karshen rikice-rikice da kuma kyautata kwarewar tinkarar bala'u daga indallahi, ta yadda za a daidaita matsalolin jin kai da ke addabar kasashen duniya.

A sanarwar da aka fitar, Mr. Guterres ya ce, gudummawar da aka bayar ba za ta kai ga biyan bukatun mutane miliyan 130 a duniya ta fannin agajin jin kai ba, don haka, ya kamata a kulla abokantaka a yunkurin magance tare da kawo karshen rikice-rikice da kyautata kwarewar tinkarar bala'u, tare da kawar da matsalar daga tushe. Mr. Guterres ya kara da cewa, ya ji dadin kokarin da aka yi wajen cika alkawuran da aka dauka a gun taron, kuma ya yi kira ga sassa daban daban da su ci gaba da wannan kokari, don kara cimma nasara a wannan bangare.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China