in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta taimakawa Gambia kafa hukumar TRC
2017-05-18 19:20:45 cri
Kungiyar tarayyar Afirka ta bayyana kudurinta na taimakawa kasar Gambia wajen ganin ta kafa hukumar tsage gaskiya da sassantawa, da nufin gano irin ta'asar da aka tafka a kasar cikin shekaru 20 da suka gabata.

Shugaban tawagar kungiyar ta AU da aka tura kasar ta Gambia Pierre Buyoyo shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan wata ganawar sirri da tawagar ta yi da mataimakiyar shugaban kasar Fatoumatta Jallow Tambajang.

Ya ce ziyarar tawagar ta mai da hankali ne kan yadda za a taimakawa kasar Gambia ta gudanar da sauye-sauye a fannin tsaro, tattalin arziki da kuma yadda za a kafa hukumar tsage gaskiya da sasantawa ta kasar(TRC)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China