in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsaron MDD ya yi Allah wadai da hari kan jami'an MINUSMA
2017-05-05 13:58:33 cri
Kwamitin tsaron MDD ya yi matukar Allah wadai da harin da aka kaiwa tawagar jami'an wanzar da zaman lafiya dake aiki a Mali ko MINUSMA a takaice, lamarin da ya hallaka jami'in tawagar daya, tare da jikkata wasu da dama.

Wata sanarwa da kwamitin na tsaro ya fitar, ta ce an kai harin wani sansanin MINUSMA dake birnin Timbuktu, abu ne mai matukar tada hankali. Tuni dai kungiyar Jama'at Nusrat al-Islam wal-Muslimin ta ce ita ce ta kaddamar da harin.

Mambobin kwamitin na tsaro dai sun ja hankalin gwamnatin Mali, da ta gaggauta gudanar da bincike game da aukuwar lamarin, tare da gurfanar da wadanda suka kitsa shi gaban kuliya, suna masu bayyana harin, a matsayin laifin da ka iya zama na yaki a karkashin dokokin kasa da kasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China