in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika zata samu kyakkyawar makoma idan Najeriya da Afrika ta kudu sun samu bunkasuwa
2017-05-05 10:22:07 cri
Wani jami'in kamfani ya bayyana cewa nahiyar Afrika zata samu makoma mai kyau idan biyu daga cikin manyan kasashen da suka fi karfin tattalin arziki a nahiyar suka samu bunkasuwa.

A wani taron tattaunawa da aka gudanar a a birnin Durbana yayin taron tattaunawar harkokin tattalin arziki na Afirka, Kuseni Dlamini, shugaban kamfanin Massmart Holdings yace, makomar cigaban nahiyar Afrika ya ta'allaka ne da kasashe biyu mafiya karfin tattalin arziki a nahiyar, kuma sun kasance a matsayin ginshikai wajen magance kalubalen da al'umma ke fuskanta a nahiyar.

Dlamini yace Najeriya da Afrika ta kudu gaba daya suna bada gudumowar kashi 60 cikin 100 na karfin tattalin arzikin GDP na kasashen Afrika da ke kudu da hamadar saharar, kuma Afrika ba zata iya cimma nasara ba matukar wadannan kasashen biyu basu samu nasara ba.

Geoffrey Qhena, babban jami'in kamfanin Industrial Development Corporation wato (IDC) na kasar Afrika ta kudu, ya bayyana cewa manyan kasashen biyu bai kamata su dogara wajen shigo da kayayyaki daga waje ba, sai dai a cewarsa kamata yayi su kakkafa masana'antu da kamfanoni domin amfanin kansu da sauran kasashen dake nahiyar. Yace ya kamata shugabannin su yi watsi da duk wasu bambance bambance dake tsakaninsu su hada kai wajen samar da muhimman abubuwan da zasu kawo cigaban nahiyar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China