Jaridar Sudan Tribune ta ba da rahoton cewa, fadan ya barke ne bayan da wasu mutane dauke da makamai 'yan kabilar Salamat suka yi awon gaba da shanu na 'yan kabilar Habaniya.
An ruwaito wani jami'in yankin yana cewa,an tura sojoji don raba sassan biyu tare kuma da hana aukuwar fadan a nan gaba.
Bayanai na cewa, tsawon shekarun da aka dauka ana kokarin kawo karshen fadan kabilanci a yankin ya ci tura, lamarin da ke haifar da damuwa ga mazauna da ma hukumomin yankin dake fama da tashin hankali.
Matsalolin tsaro da yadda kabilun yanki ke rike da makamai da rashin kyakkyawan shugabanci a galibin yankunan dake shiyyar, suna daga cikin abubuwan dake haddasa tashin hankali a yankin na Darfur.