in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwarraru a nahiyar Afrika sun yi gargadin cewa, rage tallafin da Amurka ke badawa zai yi illa ga shirye-shiryen raya nahiyar
2017-04-29 13:06:47 cri
Kwararru a nahiyar Afrika, sun ce sabon tsarin Amurka na rage tallafin da take badawa ga kasashen waje, zai yi illa ga aiwatar da shirye-shiryen rage talauci da ciyar da tattalin arziki gaba da tabbatar da zaman lafiya da kare muhallin rayuwar hallitu a yankin kudu da hamadar sahara.

A wani bangare na taron cibiyar inganta noman masara da alkama ta duniya, Daraktan shirin noman masara na cibiyar, Boddupali Prassana, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, gwamnatocin nahiyar Afrika ba su da wata mafita, illa su sake sauya inda suka sa gaba, domin tunkarar manufar Washington na rage kudin da take bayarwa ga gudanar da harkokin nahiyar.

A baya-bayan nan ne shugaba Donald Trump, ya sanar da rage yawan kudaden da ake warewa hukumar raya kasashe ta Amurka wato USAID.

Idan aka aiwatar da wannan sabon tsarin, ana sa ran zai yi mummunan tasiri ga kasashe masu tasowa, la'akari da yadda hukumar ke taimakawa shirye-shiryen samar da ci gaba a kasashen Afrika 30.

Sai dai, umarnin ba zai shafi kudaden da ake warewa na yaki da cutar kanjamau ba, amma kuma, zai shafi shirye-shiryen tallafawa bincike a fannonin harkokin noma da sauyin yanayi a yankin kudu da hamadar Sahara. (Fa'iza Musatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China