in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bayyana damuwa game da shirin Amurka na girke na'urorin THAAD a Koriya ta kudu
2017-04-26 20:21:15 cri
Kasar Sin ta bayyana damuwarta game da shirin kasar Amurka na girke na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin Thaad a kasar Koriya ta kudu, ganin yadda tuni wani bangare na na'urorin suka isa Koriya ta kudun.

A saboda haka kasar ta bukaci kasashen Koriya ta kudu da Amurka da su janye na'urorin kana su dakatar da jigilar ragowar wadannan na'urori.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a yau Laraba, ya kuma bayyana cewa, girke na'urorin babu abin da zai haifar illa kara dagula al'amura a yankin, tare da kara tsanta halin da ake ciki a zirin koriya. Kuma hakan ba zai taimaka a kokarin da ake na kawar da makaman nukiliya a zirin ba, baya ga kara kawo barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China