in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwararre:Samar da kudade kadai ba zai kawar da zazzabin cizon sauro a Najeriya ba
2017-04-25 20:22:44 cri
Shugaban cibiyar sashen yaki da zazzabin cizon sauro da dakin gwaje-gwaje na asibitin zumunta tsakanin Sin da Najeriya Okechukwu Ezekwesili ya bayyana cewa, samar da kudade kadai ba zai wadatar ba, a yakin da ake yi na kawar da zazzabin cizon sauro a Najeriya.

Jami'in wanda ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Abuja, fadar mulkin Najeriya, gabanin ranar yaki da zazzabin cizon sauro na duniya da aka saba gudanarwa ranar 25 ga watan Afrilun kowace shekara, ya ce muddin ana bukatar kawar da cutar baki daya, kamata ya yi gwamnati da al'umma baki daya su hada kai domin tsaftace muhallinsu maimakon su dogara ga maganin cutar kadai.

Mr Okechukwu ya kara da cewa, wajibi ne a fara tsaftace muhalli, wadda ke zama matattarar sauro, a matsayin matakin farko na kawar da cutar ta Malaria. Ya ce idan har aka samu nasarar yin haka,kusan za a magance kashi 50 cikin 100 na cutar.

Ya ce,ko da ya ke samar da kudaden yana da muhimmanci a kokarin ganin bayan wannan cuta,amma babu wata nasarar da za a cimma ko da an samar da biliyoyin dalaloli a tsarin kiwon lafiya, idan jama'a ba su tsaftace muhallinsu ba.

Taken ranar yaki da cutar zazzabin cizon sauro na bana da hukumar lafiya ta duniya ta ayyana, shi ne kawo karshen cutar ta malaria kwata-kwata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China