in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 7 sanadiyyar faduwar wayar wutar lantarki
2017-04-22 12:39:24 cri
Rundunar 'yan sandan jihar Delta dake kudancin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 7 tare da jikkatar wasu 11, sanadiyyar faduwar wayar wutar lantarki kan magoya bayan kwallon kafa a lokacin da suke kallon wani wasan kwallo.

Al'amarin ya auku ne a wani gidan kallo a Calabar babban birnin jihar Cross River a ranar Alhamis, da misalin karfe 9:30 na dare agogon Nijeriya, a lokacin da ake qasar kwallon kafa na nahiyar Turai tsakanin kungiyoyin Manchester United da kuma Anderlecht.

Kwamishinan 'yan sandan jihar Hafiz Inuwa ne ya tabbatar da aukuwar hatsarin, yayin wani taron manema labarai da ya kira jiya Jumma'a a Calabar.

Hafiz Inuwa, ya ce kiran taron manema labaran ya zama wajibi, la'akari da yadda wasu jaridun kasar da masu rubutu a shafin intanet ke cewa mutane sama da 30 ne suka rasa rayukansu yayin hatsarin.

Ya ce a hakikanin gaskiya, mutane 18 ne al'amarin ya rutsa da su, kuma an garzaya da su asibitin koyarwa na Jami'ar Calabar.

A nata bangare, hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta bayyana alhinin mutuwar magoya bayan kwallon kafar na birnin Calabar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China