in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
 Kasar Sin da kasashen Afrika za su hada hannu wajen yaki da cutar Malaria
2017-04-22 12:32:27 cri
Kasar Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen sake inganta yaki da cutar Malaria, ta hanyar gudanar da bincike kan kwayoyin cututtuka da horas da jami'an kiwon lafiya da kuma samar da magunguna masu rahusa.

Sakataren ma'aikatar lafiya na Kenya Cleopa Mailu ne ya bayyana haka, yayin wani taron karawa juna sani kan yaki da cutukan lokacin zafi da ma'aikatar lafiya ta kasar Kenya da hadin gwiwar hukumar samar da magungunan gargajiya na kasar Sin da kuma jami'ar nazarin magungunan gargajiya ta Guangzhou suka shirya.

A jawabinsa yayin bude taron, Cleopa Mailu ya yabawa kasar Sin bisa gudunmawar da take bayarwa wajen yaki da cutar malaria da ke sanadin rayukan yara da mata masu juna biyu a Afrika.

Ya kara da cewa, suna jinjinawa masana kimiyya na kasar Sin da suka gano sinadaran hada maganin Artemisinin, wanda ya zo a lokacin da maganin cutar malaria ke kokarin zama kalubale ga duniya.

Ya kuma bayyana cewa, ingantattun masana'antun samar da magunguna na kasar Sin sun ba kasashen Afrika kwarin gwiwar samar da magunguna da kansu tare da inganta hanyoyin tunkarar cutukan kokacin zafi masu kisa.

Har ila yau, Cleopa ya ce a shirye kasashen Afrika suke, su yi amfani da magungunan gargajiya na kasar Sin wajen yakar cutar malaria da aka dorawa alhakin asarar kaso 1.5 na tattalin arzikin kasashen da cutar ta fi kamari. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China