in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a sake bude filin jirgin saman Abuja bayan kammala gyara shi
2017-04-19 10:43:03 cri
A yau Laraba za a sake bude filin jirgin saman Abuja helkwatar Najeriya bayan kammala aikin gyare gyare.

Shugaban hukumar kula da sufurin jiragen sama na kasar ya tabbatar da cewa aikin gyare gyaren da aka gudanar na tsawon makonni 6 ya kammala tsab, kuma aikin ya cika ka'idojin hukumar lura da sufurin jiragen sama ta kasa da kasa (ICAO) kuma sun gamsu da aiki.

Jami'in yace a halin yanzu jiragen saman zasu iya cigaba da sauka ko tashi daga filin jirgin saman.

A ranar 8 ga watan Maris ne gwamnatin Najeriya ta bada sanarwar rufe filin jiragen saman na Abuja na wucin gadi, domin gudanar da gyaran titunan filin jirgin, wanda ya kamata a gyara su bayan yin amfani dasu na tsawon shekaru 20, amma an shafe sama da shekaru 34 ana amfani da su ba tare da gudanar da gyaran ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China