A wata sanarwar da aka rabawa manema labarai, ma'aikatar harkokin cikin gidan ta ayyana Mahmoud Hassan Mubarak daga birnin Suez, da cewa shi ne ya kitsa harin.
An haifi mutumun ne a ranar 28, ga watan Satumbar 1986 a Qena na kasar ta Masar, kuma ya taba yin aiki da kamfanin manfetur na kasar.
A ranar Lahadi ne, wasu tagwayen boma bomai suka tashi a cocin dake lardin Gharbiya da lardin Alexandria a arewacin kasar Masar, inda mutane 45 suka mutu, sannan wasu 120 suka samu raunuka.