in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara daukar matakai don kiyaye mulkin kanta da kuma tsaronta
2017-04-12 20:42:43 cri
Kwanan nan, yayin da Dalai Lama na 14 ke gudanar da harkokinsa a sassan da ake takkadama a kai, dake kan iyakar kasashen Sin da Indiya, ya sake sukar gwamnatin kasar Sin, dangane da sabanin ra'ayin da ke tsakaninsa da gwamnatin kasar Sin a kan batun akidar sake-halitta da ke da alaka da mukamin addini na Dalai Lama, da kuma batutuwan da suka shafi Tibet.

A daya hannun kuma, akwai kuma wasu jami'an Indiya dake furta kalaman da ba su dace ba dangane da batun kan iyakar. A game da wannan, a yau Laraba, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Lu Kang ya bayyana cewa, tuni gwamnatin kasar Sin ta bayyana rashin jin dadin ta ga kasar Indiya, kuma za ta kara daukar matakai don kiyaye ikonta da tsaronta.

A gun taron manema labarai da aka kira a wannan rana, Lu Kang ya ce, wannan ziyarar da Dalai Lama ke yi, ta wuce abin da bangaren Indiya ke bayyanawa a matsayin aikin da ya shafi addini. Kuma matakin na Indiya ya saba wa alkawarin da gwamnatin kasar ta dauka game da batun Tibet, kuma zai haifar da illa ga shawarwarin da Sin da kuma Indiyan ke yi, a kokarin daidaita takkadama da ke tsakaninsu kan batun yankunansu. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China