in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da mataimakiyar firaministan kasar Namibiya kuma ministar harkokin wajen kasar
2017-04-12 10:16:35 cri

Jiyar Talata ne Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da Netumbo Nandi-Ndaitwah, mataimakiyar firaministan kasar Namibiya kuma ministar harkokin wajen kasar wadda ke ziyarar aiki a birnin Beijing, hedkwatar mulkin kasar Sin.

A yayin ganawar, Wang Yi ya ce, kasar Sin na son zurfafa hadin gwiwar moriyar juna a tsakaninta da kasar ta Namibiya, da kara yin mu'amalar al'adu, da taimakawa juna a al'amuran kasa da kasa da na shiyya-shiyya, a kokarin bunkasa huldar da ke tsakaninsu daga dukkan fannoni.

A nata bangaren, Netumbo Nandi-Ndaitwah ta ce, kasarta ta yi fatan kara cin gajiyar aiwatar da sakamakon da aka samu a yayin taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka. Ta kuma yi maraba da kamfanonin kasar Sin, ciki har da masu zaman kansu da su zuba jari da habaka cinikinsu a Namibiya, tare da shiga ayyukan raya kasa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China