in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zabtarewar kasa ta kashe mutane 314 a Kolumbiya
2017-04-09 14:06:23 cri
Hukumar kiwon lafiya ta kasar Kolumbiya ta bayyana a jiya Asabar cewa, bala'in zabtarewar kasa da ya afkawa birnin Mocoa na jihar Putumayo dake kudu maso yammacin kasar, ya yi ajalin mutane 314, ciki har da yara kanana 106.

Ma'aikatan ceto sun ce, za su ci gaba da gudanar da aikin ceto zuwa gobe 10 ga wata.

Shugaban kasar Kolumbiya Juan Manuel Santos Calderon, ya isa birnin Mocoa jiya, inda ya tabbatar da cewa, za'a farfado da samar da wutar lantarki ga yankunan dake fama da bala'in cikin mako guda, kana nan da wata guda, za'a samar da wadataccen ruwa ga mutanen da bala'in ya shafa.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China