in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta ce kungiyar Boko Haram ta tilastawa wani matashi leken asiri a wasu kasuwanni tare da kashe mutane da kungiyar ta yi garkuwa da su
2017-03-29 13:32:08 cri
Hukumar tsaro da wanzar da zaman lafiya ta Civil Defence a Nijeriya, ta fara bincike kan wani matashi mai shekaru 17 da ake zargin dan kungiyar tada kayar baya ne, wanda aka kama a lokacin da ya je leken asiri a wasu kasuwanni masu cunkuso a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Shugaban rundunar tsaron Nijeriya a Jihar Borno, Ibrahim Abdullahi da ya bayyana haka, ya ce kwamandan kungiyar Boko Haram ne ya ba yaron umarnin shiga wasu kasuwanni domin leken asiri.

Ibrahim Abdullahi ya ce yayin da yaron yake bada bayanai, ya ce an tilasta masa kashe wasu mutane 13 da kungiyar ta yi garkuwa da su.

Ya kara da cewa, Kungiyar Boko Haram ta kama shi ne shekaru uku da suka gabata, inda aka ajiye shi a wani daji dake garin Kalabalge na jihar Borno.

Har ila yau, yaron ya shaidawa jami'an tsaro cewa, sama da yara 500 da suke kai daya ne kungiyar ta horas a matsayin sojoji. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China