in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin tsakiya: Lashe zaben Lam Cheng Yuet-ngor ya cika dukkan sharruda
2017-03-26 15:31:02 cri
Mai magana da yawun hukumar dake kula da al'amurran mulki ta Hong Kong da Macao ya sanar a yau Lahadi cewa, an gudanar da zaben babbar jami'a mai kula da harkokin mulki ta yankin Hong Kong mai cin gashin kai HKSAR bisa adalci, kana zaben sabuwar jami'ar ta HKSAR ya cika dukkan sharrudan da doka ta amince da su.

Lam Cheng Yuet-ngor ta yi nasarar lashe zabe karo na biyar wanda aka gudanar a yau a matsayin babbar jami'a mai kula HKSAR.

Kakakin hukumar ya ce an gudanar da zaben cikin lumana da kwanciyar hankali, kuma zaben ya cika dukkan ka'idojin da hukumar gudanarwa ta HKSAR ta gindaya, wanda ya yi daidai da matakin da kwamitin gudanarwa na majalisar dokokin kasar Sin ya tanada. Da kuma dokokin na HKSAR, wanda ya kunshi yin zabe a bayyane, mai adalci da kuma gaskiya.

Bugu da kari, ofishin tuntuba na gwamnatin tsakiya a yankin Hong Kong mai cin gashin kai, HKSAR ya taya Lam Cheng Yuet-ngor murnar lashe zaben da aka yi karo na biyar a Hong Kong a yau Lahadi. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China