in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Likitar kasar Kenyan zata bunkasa magungunan kasar Sin
2017-03-22 12:51:39 cri
Wata likita 'yar kasar Kenya da ta samu horo a kasar Sin tace tana kokarin bunkasa hanyoyin amfani da magungunan kasar Sin a kasar ta Kenya.

Dr. Mwamaka Sharifu, wadda a halin yanzu take karatun digirinta na uku a bangaren kiwon lafiyar mata masu juna da cutukan da suka shafi mata a kolejin kiwon lafiya ta Tongji a jami'ar kimiyya da fasaha ta Huazhong ta kasar Sin, ta shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Nairobi cewa, magungunan kasar Sin suna da matukar amfani idan aka kwatanta da wasu magungunan da ba irinsu ba.

Sharifu ta fadi hakan ne a lokacin bikin miki tallafi daga gidauniyar Sino-Africa Firefly Charity ga wadanda suka gamu da ibtila'in gobara a Kibera slums.

A lokacin bikin ne kuma aka baiwa Sharifu mukamin jakadar gidauniyar bada tallafin ta Sino-Africa Firefly Charity.

Ta ce zata yi amfani da wannan dama wajen kara karfafa dangantakar dake tsakanin Sin da Afrika.

Sharifu ta ce magungunan kasar Sin sun fi tasiri a kasar ta Kenya a halin yanzu, saboda suna aiki sosai wajen warkar da cututtuka wadanda ba'a daukarsu daga wasu wadanda kuma ake yawan samun karuwarsu.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China