An ce, 'yan sandan sun kama mutane 60 da ake zaton 'yan kungiyar IS ne a birnin Ankara, babban birnin kasar, wadanda akasarinsu 'yan kasashen waje ne. Har wa yau, an kama wasu 30 a lardin Konya da ke tsakiyar kasar, tare kuma da wasu 10 a lardunan Manisa, da Istanbul, da Samsun da Gaziantep.