in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin ta fitar da takardarta ta farko a shekarar 2017
2017-02-06 09:59:22 cri
A jiya Lahadi, kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, tare da majalisar gudanarwar kasar, suka fitar da wata takardar da ke kunshe da wasu shawarwari, game da yin gyare-gyaren aikin gona, domin samar da kuzari na bunkasa ayyukan gona da raya kauyuka. Takardar da ta yi nuni da cewa, ya kamata a kara kudin shigar manoma, da inganta kayayyakin gona da ake samarwa, da kyautata tsarin aikin gona, ta yadda za a kara bunkasa harkar noma.

Wannan ya kasance karo na 14 da gwamnatin kasar Sin ta fitar da takardarta ta farko, da ta shafi harkokin raya kauyuka da aikin gona, da kuma bunkasa rayuwar manoma tun bayan da aka shiga sabon karni.

Takardar ta kuma jaddada cewa, bunkasa gyare-gyaren tsarin aikin gona, na bukatar wani dogon lokaci, ana kuma bukatar a daidaita huldar da ke tsakanin gwamnati da kasuwanni, da kuma daidaita moriyar sassa daban daban. Don haka ta ce kamata ya yi a fuskanci kalubalen da aka sanya gaba, don ingiza gyare-gyaren. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China