in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF ta kaddamar da asusun neman dala biliyan 3.3 don tallafawa kananan yara a fadin duniya
2017-02-01 12:58:16 cri

Asusun tallafawa kananan yara na MDD (UNICEF) a jiya Talata, ya kaddamar da shirin neman dalar Amurka biyan 3.3 domin bayar da taimakon gaggawa ga yara kanana a kasashen duniya 48, sakamakon yawaitar yara kanana dake hasarar muhallansu a sanadiyyar tashe tashen hankula da bala'u daga indallahi da kuma sauyin yanayi a fadin duniya.

Cikin wata sanarwa da ta fitar, MDD tace a kalla yara miliyan 48 da matsalolin suka fi shafa ne ake saran zasu ci gajiyar wannan shirin bada agajin gaggawar na hukumar ta UNICEF a shekarar nan ta 2017, wanda aka kaddamar daga ranar 31 ga watan Janairun wannan shekara.

An yi kiyasin daya daga cikin hudu na yaran duniya suna rayuwa a kasashen da rikici ko bala'u suka shafa.

UNICEF ta bayyana fargabar cewa yara kusan miliyan 7.5 ne zasu iya fuskantar matsalar matukar karancin abinci mai gina jiki a kasashen duniya da matsalar ta shafa, kuma kananan yara kusan rabin miliyan ne suna arewa maso gabashin Najeriya da kasar Yemen.

Sai dai har yanzu akwai sarkakiya, sakamakon rashin tantance alkaluma a yankin tafkin Chadi saboda rashin samun damar shiga yankin sakamakon fargabar hare haren mayakan Boko Haram. Sashen bada agajin jin kai na hukumar ta UNICEF ya kaddamar da gidauniyar neman taimakon ne na 2017, domin gudanar da muhimman ayyuka da suka shafi tallafawa kananan yara da ruwan sha mai tsabta, abinci mai gina jiki, ilmi, kiwon lafiya, da kuma baiwa yaran kariya daga barazanar hare hare a kasashen da matsalar tafi kamari.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China