in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco ta koma kungiyar Tarayyar Afrika AU, shekaru 33 bayan ficewarta
2017-02-01 12:35:11 cri

Bayan shafe shekaru sama da talatin da ficewa daga kungiyar AU, Morocco ta sake komawa a jiya Talata, yayin babban taron kungiyar karo na 28

Sama da shekaru talatin ke nan, da Kasar Morocco ta fice daga kungiyar AU wadda a lokacin ake kira da OAU, sai dai a baya-bayan nan, kasar ta sauya matsayarta, inda ta sanya komawa cikin kungiyar cikin muhimman manufofinta.

Yayin bikin rufe taron da ya gudana a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, Sarkin Morocco Muhammad na VI ya bayyanawa shugabannin na Afrika farin cikinsa na kasancewarsu tare, yana mai cewa ya yi kewarsu.

A cewarsa, duk da Morocco ta fice daga Kungiyar AU, cikin wadancan shekaru, ta kulla alaka mai karfi da galibin kasashen Afrika.

Sarki Muhammad na VI, ya kuma yi alkawarin aiki tare da sauran kasashe mambobin kungiyar, da nufin tabbatar da al'ummar Afrika sun ci moriyar arzikin dake nahiyarsu. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China