in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Filin jirgin saman kasar Masar ya hana wani iyalin Iraqi tashi zuwa kasar Masar
2017-01-29 12:39:38 cri
A jiya ne hukumomin filin jiragen saman kasar Masar suka hana wani iyali daga Iraki tashi daga filin jiragen saman na Masar zuwa kasar Amurka.

Wannan mataki na zuwa ne kwana guda bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da iznin hana musulmi daga kasashe bakwai shiga kasar.

Wata majiya daga filin jiragen saman kasar ta Masar ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa,wannan mataki wani bangare ne na bukatar da mahukuntan kasar Amurka suka gabatarwa kamfanin jiragen kasar Masar, sai sun gabatarwa bangaren Amurkar sunayen fasinjojin da ke son shiga Amurka kafin daga bisani Amurkar ta yanke shawara a kai, kuma wannan mataki ya shafi dukkan kasashen duniya.

Majiyar ta kuma bayyana cewa, an haramtawa iyalan kasar ta Iraki da 'yayansu guda biyu tashi daga Masar zuwa kasar ta Amurkan ne saboda, kasar ta Iraki tana cikin jerin sunayen kasashen da Amurka ta haramtawa 'yan kasarta shiga kasar Amurka.

A ranar Jumma'a ce shugaba Donald Trump na Amurka ya sanya hannun kan dokar shugaba, wadda ta dakatar da baiwa musulmi daga kasasahen Syria, Iraki,Yemen,Libya,Sudan, Somaliya da Iran iznin shiga kasar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China