in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD zai yi kira da kulla sabuwar dangantaka tsakanin Majalisar da Tarayyar Afrika
2017-01-26 10:47:36 cri
Kakakin Sakatare Janar na MDD Stephane Dujarric ya ce Sakatare Janar Antonio Guterress, zai yi kira da kulla sabuwar dangantaka tsakanin MDD da Tarayyar Afrika.

Dujarric ya bayyana cewa, Sakatare Janar din zai bar birnin NewYork a gobe Juma'a, domin halartar babban taron Tarayyar Afrika karo na 28, da za a yi a Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha.

Ya ce sakon Sakatare Janar din ga Tarayyar Afrika, zai mai da hankali ne wajen kulla sabuwar dangantaka cikin mutuntawa da goyon bayan juna, da kuma batutuwan da suka shafi muradun karni masu dorewa.

Ana kuma sa ran Guterres zai gana daya bayan daya da wasu shugabannin kasashen da za su halarci taron, daga bisani kuma ya tattauna da ma'aikatan MDD dake aiki a kasar Habasha. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China