in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da zaben shugaban kasar Somali a ranar 8 ga watan Fabrairu
2017-01-26 10:23:05 cri
Sabon kwamitin hadin gwiwa da majalisun dokokin kasar Somali suka kafa wanda zai jagoranci gudanar da zaben kasar, ya sanar a jiya Laraba cewa, a ranar 8 ga watan Fabrairu ne za a gudanar da zaben shuagban kasar.

Shugaban hukumar gudanar da zaben shugaban kasar Abdirahman Dualeh Beileh, ya fada cikin wata sanarwa cewa, za a fara yin rajistar 'yan takarar shugabancin kasar ne tun daga yau Alhamis har zuwa ranar Lahadi mai zuwa.

Beileh yace 'yan takarar zasu gabatar da jawabai a gaban majalisun dokokin kasar daga ranar 2 zuwa 5 ga watan Fabrairu, kana a gudanar da zaben shugaban kasar a ranar 8 ga watan Fabrairun.

Majalisar dokokin Somalia zata zabi shugaban kasar ne , kamar yadda dokar kasar ta bada dama ga 'yan majalisar su zabi wanda zai ja ragamar shugabancin kasar, zaben wanda da farko a shirya gudanar da shi a watan Satumba da Oktoba da Nuwamba daga karshe aka shirya yinsa a ranar 28 ga watan Disambar shekarar 2016, amma duk bai kai ga nasara ba.

A yanzu dai kwamitin shirya zaben kasar zai yi wasu muhimman taruka biyu a ranakun 30 ga watan Janairu da kuma 6 zuwa 7 ga watan Fabrairu, domin nazartar hanyoyin aiwatar da zaben shugaban kasar. A kalla sanatoci 17 da 'yan majalisar dokokin kasar ne aka zaba wadanda zasu halarci zaman tare da kwamitin shirya zaben.

Kasashen duniya da dama sun yi ta kiraye kirayen a gudanar da sahihin zaben shugaban kasar kuma mai inganci.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China