in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Najeriya zata binciki bullar cutar murar tsuntsaye
2017-01-26 09:42:06 cri
A jiya Laraba majalisar wakilan Najeriya ta gabatar da bukatar gudanar da bincike game da sake bullar cutar murar tsuntsaye a wasu sassan kasar.

Tuni dai majalisar wakilan Najeriyar ta kafa wani kwamiti wanda zai gudanar da bincike game da dalilan dake haddasa bullar cutar da kuma yadda za a shawo kanta, kana kwamitin zai mika rahotonsa nan da makonni 6 domin daukar makatai na gaba.

Sergius Ogun, dan majalisar wakilan kasar ne, shine ya sanar da wannan batu , inda ya bayyana damuwa kan bullar cutar wanda tuni ta bazu a jahohin kasar 26 da kuma birnin tarayya.

A cewarsa, matsalar bullar cutar ta haifar da gagarumar hasara ga masu kiwon kaji, kuma zata iya zama barazana ga lafiyar masu amfani da naman kajin.

Dan majalisar yace matukar ba a kai ga gano musabbabin dake haifar da cutar ba, akwai yiwuwar zata iya sake bulla a nan gaba.

A kalla kaji dubu 80 ne suka kamu da cutar murar tsuntsayen a gidajen gona 45 a jahar Kano a watan Janairun shekarar 2016.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China