in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun kasar Iraqi sun kwace iko da sauran sassan gabashin Mosul
2017-01-23 10:09:37 cri
Rundanr sojin Iraqi ta ce a kokarinsu na fattatakar 'ya'yan kungiyar IS daga tungarsu ta karshe dake wajen birnin Mosul, sojoji sun kwace iko da yankunan tsakiya na gabashin birnin.

Wata sanarwar da jami'in rundunar hadin gwiwa Abdul-Amir Yarallah ya fitar, ta ce dakarun Iraqi sun kwace iko da kananan garuruwan Malayeen da Al-Bina al-Jahiz dake tsakiyar Mosul, inda suka daga totocin kasar a wasu gine-gine.

Yarallah ya ce wadannan ne yankunan tsakiyar Mosul da suka rage, wato yankin da aka fi sani da gabar kogin Tigris da ya raba birnin.

Ya kara da cewa, dakarun sun kuma kwace iko da babbar hanyar da ta hada birnin Mosul da lardin Dohuk, wanda wani sashe ne na yankin Kurdistan dake da kwarya-kwaryar 'yancin cin gashin kai.

Da wannan nasarar, dakarun Iraqi sun kwace iko da dukkanin yankin gabashin Mosul, inda yankin Rashidiyah dake wajen arewacin birnin, ya kasance yanki daya tilo dake karkashin ikon kungiyar IS.

Masana sun ce da zarar dakarun sun kwace baki dayan gabashin Mosul, za su kaddamar da wani sabon yaki kan kungiyar a yankin yammacin birnin.( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China