in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin zai kai ziyara Switzerland tare da halartar taron WEF
2017-01-10 17:53:38 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin zai kai ziyarar aiki kasar S witzerland daga ranar 15-18 ga wannan wata bisa gayyatar majalisar zartarwar tarayyar kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang wanda ya bayyana hakan yau Talata a yayin taron manema kabarai a nan birnin Beijing, ya ce a lokacin wannan ziyara, shugaba Xi zai kuma halarci taron shekara-shekara na dandalin tattalin arziki na duniya(WEF) karo na 47 wanda zai gudana a ranar 17 ga wannan watan, bisa gayyatar shugaban dandalin Klaus Scwab.

Haka kuma,a ranar 18 ga watan na Janairu, ana sa ran shugaba Xi zai kai ziyara ofishin MDD da ke birnin Geneva da hukumar lafiya ta duniya (WHO), da hedkwatar kwamitin shirya gasar wasannin Olympics da ke Lausanne dukkansu bisa gayyatar shugabanninsu bi da bi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China