Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana yau Laraba 4 ga wata a nan Beijing cewa, manzon musamman na kasar Sin mai kula da batun Sham Xie Xiaoyan, zai ziyarci birnin Geneva, da hedkwatar kungiyar Tarayyar Turai, da kasashen Turkiyya da Rasha, a wani mataki na kara azama ga yunkurin da ake yi na warware batun Sham a siyasance, ba kuma tare da wani jinkiri ba. (Tasallah Yuan)