in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun kiyaye zaman lafiya ta kasar Sin sun tashi zuwa Sudan ta Kudu
2016-12-05 14:05:19 cri
A jiya Lahadi ne, rukuni na farko da ke kunshe da dakaru 120 na bataliya ta uku na dakarun kiyaye zaman lafiya ta kasar Sin suka tashi zuwa kasar Sudan ta kudu cikin jirgin sama na MDD, don su canji bataliya ta biyu ta dakarun kiyaye zaman lafiya na kasar da tuni suka kammala aikinsu a kasar.

Bataliyar dai tana kunshe ne da dakaru 700, kuma za su tashi zuwa kasar Sudan ta kudu ne cikin rukunoni 6, inda za su gudanar da ayyukan ba da kariya ga fararen hula da ma'aikatan agajin jin kai na MDD da kuma sintiri da tsaro.

Kafin su tashi, sai da suka kwashe watanni uku suna samun horo a fannoni 22, kuma dukkan dakarun sun ci jarrabawar da aka yi musu, kuma suna da kwarewa a fannin samar da tsaro.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China