A wani labarin kuma, shugaba Najeriyar ya yi kira ga kungiyoyin kabilu masu dauke da makamai da ke neman ballewa da su kwana da sanin cewa,ba mai raba Najeriya.(The Punch)
A jiya ne masana harkar tsaron zirga-zirgar jiragen sama suka yi gargadin cewa,akwai yiwuwar kai hare-haren ta'addanci a filayen saukar jiragen saman kasar, fiye da yadda hukumomin suke zato.
Kwararrun sun bayyana haka ne, bayan labarin gano gawar wani mutum da ya yi satar shiga jirgin saman Arik Air(The Guardian)