in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Muhimmancin taron COP22 ga matsalar sauyin yanayin duniya
2016-11-25 16:42:33 cri

A ranar Jumma'a 5 ga watan Nuwamban shekarar 2016 ne babban sakataren MDD Ban Ki-moon da wakilan kungiyoyin al'ummomi suka shirya taron karawa juna sani domin murnar fara aiki da yarjejeniyar sauyin yanayi da aka cimma a birnin Paris na kasar Faransa a hukumance.

Bugu da kari, a ranar 7 ga watan na Nuwamba ne aka fara taron kwanaki 11 na kasashen da suka sanya hannu kan wannan yarjejeniya a birnin Marrakech na kasar Morocco. Yanzu haka dai kasashe kimanin 100 ne suka sanya hannu kan wannan yarjejeniya.

A watan Disamban shekarar 2015 ne aka amince da yarjejeniyar a birnin Paris na kasar Faransa. Kana a watan Oktoban shekarar 2016 da muke ciki, kasashe 96 da kungiyar tarayyar Turai (EU) suka sanya hannu a kanta, daga bisani kuma yarjejeniyar ta fara aiki a ranar 4 ga watan Nuwamban wannan shekara.

Masana dai na nuna cewa, duk irin sakamakon da za a samu ko aka samu a yayin manyan tarukan tinkarar sauyain yanayi na duniya za su yi tasiri matuka ga 'yancin kowane mutum game da neman samun ci gaba a duniyarmu.

Masu fashin baki na ganin cewa, batun tinkarar sauyin yanayin duniya, ba batu ne na siyasa ba kawai, wannan al'amari ne na tattalin arziki. Don haka, muddin ana bukatar yarjejeniyar ta taka rawar da ta dace a kokarin da ake yi na magance matsalar sauyin yanayin duniyar da muke ciki, wajibi ne kasashe da kungiyoyin da abin ya shafa su cika alkawarin da suka dauka daga dukkan fannoni. (Ada, Saminu, Ibrahim/Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China