Shugaban ya basu tabbacin samun zaman lafiya da kyakkyawan yanayin kasuwanci a kasar, gabanin gudanar da babban zaben kasar dake tafe a watan gobe, wanda shugaba Mahama ke sake yin takarar neman zarcewa a shugabancin kasar.
Game da koma bayan tattalin arziki dake addabar duniya kuwa, shugaban yace, kasar Ghana ta samu nasarori masu yawa wajen kaucewa fuskantar matsin tattalin arziki, inda ta sha gaban kasashen duniya da dama, ya kara da cewa, kasar na cigaba da daukar matakan da suka dace domin kaucewa fadawa cikin tabarbarewar al'amurra.( Ahmad)