in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Al'ummar Koriya ta Kudu sun yi taron gangami don bukatar shugabar kasar ta yi murabus
2016-11-13 13:32:44 cri
Dubun dubantar al'ummar kasar Koriya ta Kudu sun yi taron gangami a jiya Asabar a Seoul, babban birnin kasar, inda suka bukaci shugabar kasar Park Geunhye da ta yi murabus nan da nan a sakamakon batun sa hannu cikin harkokin mulki da kawarta ta yi. A cewar kafofin yada labarai na kasar, taron gangamin ya kasance mafi kasaita tun daga shekarar 2000.

A wannan rana, shugabannin manyan jam'iyyun adawa uku na kasar sun halarci wannan taron gangamin.

A labarin da aka bayar, ban da birnin Seoul, al'ummar kasar da ke biranen Busan da Jeju da sauransu ma sun yi zanga-zanga ko gangami don bukatar shugabar ta yi murabus.

Manazarta suna ganin cewa, babban taron gangami da aka gudanar a wannan rana ya sake bayyana rashin jin dadin al'umma ga gwamnatin Park Geunhye.

A binciken da Gallup Korea ya gudanar, an ce, a cikin watan nan na Nuwanba, yawan goyon bayan da aka nuna wa shugaba Park Geunhye ya kai kimanin kashi 5% kawai a cikin makwanni biyu a jere, adadin da ya kai wani matsayi mafi kankanta a tarihin shugabannin kasar.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China