in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar AU na bincike kan zarge zargen kisan fararen hula a Somaliya
2016-11-13 13:20:39 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta kungiyar tarayyar Afrika dake Somaliya (AMISOM) ta sanar a ranar Asabar cewa ana gudanar da wani bincike kan bayanan dake nuna cewa akwai yiyuwar dakarunta sun kashe a kalla fararen hula 7 a tsakiyar Somaliya bayan wani gumurzu a ranar Laraba tare da mayakan kungiyar Al-Shabaab.

Tawagar AU ta bayyana cewa wani ayarinta dake kan hanyar zuwa Ceel Buur ya murkushe wani kwanton bauna da mayakan Al-Shabaab suka shirya da kuma janyo babbar asara ga mayakan 'yan ta'adda.

AMISOM nada labarin wadannan zarge zarge na kafofin yada labarai kan mutuwar fararen hulan din a cikin dukkan ayyukansu, inda ta kara da cewa dukkan wadannan zarge zarge an yi bincike kansu tare da hukumomin Somaliya.

A cewar kafofin yada labarai, fararen hula 7 ne sojojin Habasha suka harbe a lokacin da suke aiki a cikin tawagar AMISOM. Wadannan labarai sun tabbatar da cewa dakarun AU sun yi barin wuta a yankin Dac, bayan da mayakan kungiyar Al-Shabaab suka yi musu kwanton bauna a birnin dake tsakiyar Somaliya.

Mayakan Al-Shabaab sun kara zafafa hare harensu a 'yan watannin baya bayan domin kifar da gwamnatin Somaliya da kafa wata kasar dake aiki da dokokin musulunci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China