in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta jaddada goyon bayan ta ga yaki da Boko Haram
2016-11-11 20:20:57 cri
Kwamishinan kungiyar AU mai kula da harkokin tsaro da zaman lafiya Smail Chergui, ya ce AU za ta ci gaba da goyon bayan yakin da ake yi da kungiyar nan ta Boko Haram, karkashin tawagar hadin gwiwar dakarun wasu kasashen yammacin Afirka ko MNJTF a takaice. Mr Chergui ya bayyana hakan ne yayin wani taron manyan dakarun sojojin tawagar wanda ya gudana jiya Alhamis.

Wata sanarwa da aka fitar bayan taron, ta nuna cewa mahalartan sa sun maida hankali ga tattauna yanayin tsaro da ake ciki game da ayyukan tawagar, da ma sauran muhimman hanyoyin bunkasa ayyukan tawagar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China