Shahararren masanin adabin nan dan Najeriya, wanda ya lashe lambar yabo ta Nobel a shekarar 1986 Farfesa Wole Soyinka, ya yi kurarin yaga takardar shaidar sa ta zama dan Amurka, muddin Donald Trump ya yi rantsuwar kama aiki a matsayin shugabancin Amurka a ranar 20 ga watan Janairun shekarar 2017 mai zuwa.
A makon da ya gabata ne dai Soyinka, ya yi wannan kurari yana mai nuna bacin ran sa da yadda Mr. Trump din ya samu takara a babban zaben na Amurka. (The Punch)