Kungiyar Boko Haram ta kaddamar da wani hari kan wata bataliya ta 119 ta rundunar sojojin Najeriya dake yankin Malam Fatori dake jihar Borno, in ji Sani Usaman, kakakin rundunar.
Haka kuma, sojojin sun kwato wata igwa da bindigogi kirar AK-47 guda bakwai da kuma tarin alburusai masu yawa bayan gumurzun, in ji mista Sani Usaman tare da bayyana cewa sojojin kasar sun kara zafafa cigaba da aikin kakkabe yankin.
Gwamnatin Najeriya ta kaddamar da ayyukan soja da dama a tsawon 'yan watannin baya bayan nan domin kawar da kungiyar Boko Haram a yankin jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya. (Maman Ada)