in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da dandalin hadin gwiwar masana'antu tsakanin Sin da Afirka karo na farko
2016-10-31 14:03:47 cri
A ranar Asabar 29 ga wata ne, aka gudanar da babban taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar masana'antu tsakanin Sin da kasashen Afirka karo na farko a nan birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin.

A yayin taron, an gabatar da rahoto dangane da harkokin hadin gwiwar masana'antu a tsakanin lardin Zhejiang na kasar Sin da kasashen Afirka a shekarar 2016, rahoton ya samar da shawarwari masu inganci ta fannin inganta harkokin cinikayya a tsakanin lardin Zhejiang da kasashen Afirka, tare kuma da saukakawa masu masana'antu na sassan biyu yadda za su zuba jari da gudanar da harkokin kasuwanci a kasashen juna, haka kuma ya samar da shawarwari ga sauran larduna da birane na kasar Sin kan yadda za a aiwatar da hadin gwiwar masana'antu da kasashen Afirka.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China