A ranar Jumma'a 21 ga wata ne za a bude taron tunawa da cika shekaru 80 da cimma nasarar doguwar tafiya, taron da zai gudana a babban dakin taron jama'a da ke nan birnin Beijing da karfe 10 safiyar wannan rana. Babban sakataren kwamitin tsakiya na jam'iyyar JKS kana shugaban Sin kuma shugaban rundunar sojan Sin Xi Jinping zai halarci taron tare da gabatar da muhimmin jawabi.(Lami)