in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taro nn 23 na ministocin kudi na kungiyar APEC
2016-10-17 10:57:05 cri
An kammala taro na 23 na ministocin kudin kungiyar hadin gwiwar kasashen dake yankin Asiya da tekun Pasifik a fannin tattalin arziki wato APEC a ranar Asabar.

Mataimakin ministan kudin kasar Sin mista Dai Baihua ne ya jagoranci tawagar kasar Sin wajen halartar taron. A jawabin da ya gabatar, Mr. Dai ya bayyana cewa, yankin Asiya da tekun Pasifik ya kasance daya daga cikin yankunan da ke samun ci gaban tattalin arziki mafi sauri a duniya. A ganinsa, nan gaba, ya kamata a daidaita tsare-tsaren tattalin arzikin kasashen Asiya da tekun Pasifik, don neman karuwar tattalin arzikin mai dorewa wanda zai amfani kowa.

Ban da haka kuma, ya kamata a inganta hadin gwiwar kasashen dake yankin a fannonin zirga-zirga, da sadarwa, da harkar kudi, da mu'ammalar al'umma, da dai sauransu. Kaza lika a kyautata muhallin zuba jari, da daidaita matsalar koma bayan kayayyakin more rayuwa, da dai makamantansu, don kara ciyar da tattalin arzikin yankin gaba. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China