in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta kalubalanci kasashen Amurka da Koriya ta Kudu game da dakatar da yunkurin girka tsarin THAAD
2016-09-30 19:53:36 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya ce, Sin ta ja hankalin kasashen Amurka da Koriya ta Kudu, da su kula da damuwar kasashen shiyyar, tare kuma da dakatar da yunkurin girke na'urorin kakkabo makamai masu linzami karkashin tsarin nan na THAAD.

Mr. Geng ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka yi a Juma'ar nan, inda ya ce Sin ta riga ta bayyana matsayinsa kan wannan batu sau da yawa. A cewarsa, girke na'urorin na THAAD a kasar Koriya ta Kudu da Amurka ke nufin aiwatarwa, ba zai kawar da damuwar bangarorin da batun ya shafa ba, kuma ba zai haifar da nasara ga cimma burin dakile makaman nukiliya a zirin Koriya ba. Kaza lika, ba zai wanzar da zaman lafiya a zirin ba.

Baya ga haka, matakin zai lahanta moriyar kasashen shiyyar ta fuskar tsaro, ciki har da kasar ta Sin, zai kuma wargaza daidaito a fannin manyan tsare-tsaren shiyyar. Don haka kasar Sin ke adawa matuka da wannan mataki. Za kuma ta dauki matakai da suka wajaba, domin kiyaye tsaronta, da kuma tabbatar da daidaiton shiyyar ta fannin manyan tsare-tsare. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China